Saturday, October 10, 2020

ZAN FARA RABA MUKU JARI DA ZARAR NA DAWO NGURU — HON. LAWAN SANI — MATA


Dan majalisa mai wakiltar Nguru ta tsakiya Hon. Lawan Sani ya tabbatar wa mata a mazabarsa cewa ya shirya tsaf domin fara raba musu jari kamar yadda ya alkawuranta musu a lokacin yakin neman zabe.

Hon. Lawan wanda ke a birnin Abuja a halin yanzu ya fada a zantawarsa da wannan Dandali ta wayar salula cewa zai fara ba wa matan jarin ne da ya dawo Nguru.

To sai dai Honarabil din ya kokwanta cewa balalle ne dukkannin alkawaran su samu ba, inda ya buga misali da wasu gaggan shugabanni da su ma ba su iya cika dukkan komai ba.

Ya ce Allah shi ke cika komai daidai, to amma ya ce zai yi iya kokarinsa wajen ganin Allah ya taimake shi ya cika su gaba daya.

Ko da wakilin Dandalin tambaye shi shin ko mai zai ce game da zargin da mutum 10 ya koma APC?  Nan take sai ya karyata zargin cikin raha, inda ya ce ko a ahalin gidansu ma wadanda ya koma da su sun fi mutane 10.

A doguwar hirarsa da wannan Dandali Hon. Lawan ya kuma yi kakkausan martani ga masu cewa sai da ya danke wasu 'yan sulalla kafin sauyin shekarsa, inda ya kalubalanci duk wani mai ikirarin hakan akan ya kawo hujja.

Yana mai tabbatar da cewa ya koma APC ne ba tare da ya gindaya ko an gindaya masa wani sharadi ba.

Wakilin wannan Dandali ya sake tambayar sa game da zargin rashin yin shawara da 'yan tsohuwar jam'iyyarsa gabanin sauyin shekarsa? Hon. Lawan sai ya kada baki ya ce, ko kadan bai yi gaban kansa ba har sai da ya naimi shawara.

Ya ce wadanda ya shawarta sun san ya yi Shawara, wadanda kuma neman bai kai gare su ba, ya ce to ka ga wadannan dole su ba a yi shawara ba kwata-kwata.

Hon. Lawan daga karshe ya gode wa masoyansa da ma daukacin al'umar Nguru, inda ya musu albishirin cewa akwai wani gagarumin gangami da za a shirya na neman gaisuwa.

Sannan kuma ya yi barazanar neman hakkinsa daga duk wanda ya yi masa yarfe ko kazafin bai ji ba bai gani ba.

Wednesday, September 30, 2020

DAN MAJALISA DAYA NA PDP A JIHAR YOBE YA KOMA JAM'IYYAR APC


Dan majalisar jiha na jam'iyyar PDP mai wakiltar Nguru ta tsakiya a jihar Yobe, Hon. Lawan Sani Inuwa, ya fice daga jam'iyyar inda ya koma jam'iyyar APC.

A Larabar nan ce dai labarin sauya shekar da hotunan dan majalisar ya game dandalin sada zumunta na galibin wadanda yake wakilta.

Batun sauya shekar Hon. Lawan Sani ya janyo cecekuce a Nguru, inda wasu ke ganin cewa sauyin shekar babu abin da za ta janyo wa dan majalisar face nadama, yayin da wasu ke ganin sauyin shekar shi ya dace.

Wani dan jam'iyyar PDP mai goyon bayan dan majalisar da ya bukaci a boye sunansa ya shaida wa wannan dandali cewa Hon. Lawan bai yi aiki da shawara ba a yayin sauyin shekarsa.

To sai dai a zantawarsa da wannan dandali a daren Larabar nan Hon. Lawan ya kwatanta sauya shekarsa da sinadarin gaskata mafarkin wadanda ake wakilta.

Hon. Lawan ya kara da cewa duk fadi-tashinsa a tsohuwar jam'iyyarsa da kuma sabuwa da ya koma shi ne domin ya ga ya cimma muradun al'umarsa gaba daya kwata.

Ya ci gaba da cewa bai fice daga jam'iyyar PDP ba zuwa APC, har sai da ya nemi shawarwari daga masana kan alheri yin hakan ko akasin haka ga mutanensa.

Ana sa ran daga gobe Alhamis ne zuwa wani lokaci za a gudanar da gangamin wankar dan majalisar a Nguru.

Da ma dai Hon. Lawan dan jam'iyyar APC ne Kafin daga bisani ya koma PDP.

Abin jira a gani dai a halin yanzu shi ne martanin jam'iyyar PDP kan sauyin shekar, tare sauraran ganin shin ko Honarabil din ya koma APC ne tare da Jama'arsa ko kuma dai shi kadai ya koma?

Tuesday, August 11, 2020

Malaman Sakandare a Yobe sun shiga aji a karan farko bayan sake bude makarantu

Mafi yawancin daliban ajin karshe na makarantun karama da babbar Sakandare a jihar Yobe a yau Talata sun koma makarantunsu, inda a wasu makarantun har aka fara gabatar musu da darussa.

A Larabar da ta gabata ne gwamnatin jihar Yobe ta ba da izinin sake bude makarantun Sakandare domin daliban ajin kashe su dauki jarabawar karshe ta WASSCE.

Wakilin wannan Dandali a yau Talata ya kewaya wasu makarantu a Nguru, ya kuma ba da labarin cewa dalibai da dama sun koma, inda har a wasu makarantu aka gudanar da darussa.

A makarantar gwamnati ta Haya Islam inda wannan Dandali ya fara ziyarta, an martaba ka'idojin matakan kariya  da gwamnatin tarayya ta dingaya.

Wani Malamin makarantar da ya bukaci a boye sunansa a zantawarsa da wannan Dandali ya nuna jin daÉ—insa da bude makarantun.

Yana mai korafin cewa tsarin da a ka yi na bitar karatuttukan yaran a cunkushe yake.

A sauran makarantu ma a garin, wasu rahotanni sun nuna cewa lamarin bai sauya ba, yayin da a wasu kuma aka samu tsaiko kafin a gama gwajin zafin jikin dalibai.

A tuna cewa, a Litinin din mako mai zuwa 17 ga watan Agusta 2020 ne daliban makarantun Sakandare a fadin kasa za su fara daukar jarabawar karshe ta WASSEC da hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma WAEC ke shiryawa.